Saturday, January 17, 2009

Wakar Mayaumasoyiya Wakar da na rubuta a Birnin Ouagadougou Burkina Faso

Daga
Comrade Rabi’u Na’auwa
Daga Birnin Ouagadougou Burkina Faso

Bissalam salama a gareki masoyiya a yau zan barki

1. Ya Allahu ya ahadu samadu
Lam ya ld walam yu ladu wahidu
Sarkin nan guda wanda yayo du
Duniya Rahimu ya kageni

2.Allahumma salli wala adadu
Wanda ba ya shi kuma har abadu
Bashi yaudara shi Muhammadu
Kinga yau mayau ni kin barni

3. Nai salati gun baban zahra
Jarumi maki gunta yaudara
Yayi tur da hali na yaudara
Amma kinka aikota gareni

4.Na iso cikin gaggawar
Domin ganinta nake sha’awar
Yan uwa kuyi mani ta’aziyar
Domin masoyiya ta barni

5.Mayaumasoyiya ta barni
gashi sonta ya kamani
Rashin sani ya kwareni
Da na barta tun tuni babu sani

Ki tuna fa ni ne mai sonki
Mai zurfafawa kan sonki
Mai yin bajintar kaunarki
Kin manta wannan kin barni

Ki tuna batun alkawarinmu
Na ranar nishadinnan tamu
Juma’a ta zamto ranarmu
A gidanku amma kika barni

Ashirin da huddu fa su na tuna
Ga augusta na san zaki tuna
Kika dauki alkawari ki tuna
Amma kinka karya kika barni

Ki tuno kalaman nan naki
Baki yaudara a kalamanki
Baki cin amanar kaunarki
Gashi kinci tawan kin barni


To gashi yau kinci amana
Ki tuno da sonmu fa na amana
Alkawar fa kaya ne ki tuna
Kin karya shi yau kin barni

Ki tunafa ni ne nassoki
Naki tanka kowa dominki
Na bayar da kaina a gareki
Hally a yau kin barni

Ki tuno da ranar soyayya
Wadda munka yita a can baya
Ki tuno nishadinmu na baya
Kin zubda shi yau kin barni

Kin butulci fannin soyayya
Kin karya darajar soyayya
Kin yaudara bisa soyayya
Tinda gashi kin yita gareni

Ki tuno nasiharki garemu
Dadi ko wuya mu rike kanmu
Mu rike amanar junanmu
Har mu cimma buri babu hani

Gashi dukka kin ture wannan
Babu kuskure daga ni dinnan
Ke kinka furta kalaman nan
Ofishinku ban manta ki sani

Zai kyau ki san son alkawari
Bashi saiduwa don dinari
Masoya kuzan cika alkawari
Ku rikeshi ba ji babu gani

Gashi na rikeshi daram ku sani
Mayaumasoyiya ce ta gujeni
Ta kareshi kal domin ku sani
Babu so a yau ta barni

Sai mu daina koyi da irinsu
Kunga duniya ta rudesu
Mu mu bita sannu fa ya nasu
Na garinmu balle yan birni

Zai kyau gaba daya muyi nazari
A duniya mu yi Alkairi
Don lahira muga alkairi
Kin manta wannan kin barni

Yanzu dai nasiha zan yi maki
Ki rike mijinnan naki
Domin ki san Aljannarki
Na gareshi ban son yai yi hani

Zaifi kyau ki san soyayya
Bata bin tunanin dukiya
Lallai mubar son zuciya
Dube misali kin gujeni

Arrahimu nai yi kira Jalla
Ka haneni yaudara duk wahala
Ka tsaremu fadawa wahala
Don Hally yau ta barni

Gani yau a Burkina ba wahala
Wagaduggu naccika su jumla
Baitocinga sun ka zamo jumla
Ashirin da huddu ku zamfa sani

Alhamdu Jalla gwani nawa
Da ka bani ikonjurewa
Na yi baituka ga mayau tawa
Da ta yaudareni ta cuceni.

No comments:

Post a Comment